Alhamis 6 Agusta 2026 - 20:59
Tattakin Arba’in na Bana ya Bayyana Tsantsar Ƙaunar Al’ummar Musulmi ga Shahidin Jagora

U Hauza/ Wakilin Waliyyul Faƙih kan harkokin Hajji da Ziyara ya bayyana cewa Tattakin Arba’in na bana ya kasance wata alama ta tsantsar ƙaunar al’ummar Musulmi ga Shahidin Jagora.

A cewar rahoton wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Hujjatul Islam wal Muslimin Sayyid Abdul-Fattah Nawaab, Wakilin Waliyyul Faƙih kan harkokin Hajji da Ziyara, a ƙarshen tafiyarsa ta Arba’in wadda ya yi domin inganta hidimar da ake yi wa maziyartan Arba’in, da kuma ganawa da masu kula da Haramai Masu Tsarki, malamai da maraji’an Iraki, tare da ziyartar masu hidimar Arba’in, ya bayyana a wata hira da manema labarai cewa: "Muna gode wa Allah Maɗaukaki da Ya ba ƙaunatacciyar al’ummar Iran damar ci gaba da kasancewa a fage da tituna, tare da nuna cikakkiyar halartarsu a Arba’in na Imam Husaini, wannan lamari na musamman da ba ya da tamkarsa a zamaninmu; wani lamari ne da Shahidin Jagora yake ba shi muhimmiyar kulawa, kuma a ko da yaushe yana jaddada gudanar da shi yadda ya kamata. A bana, an gudanar da wannan biki cikin mafi kyawun yanayi."

Ya ƙara da cewa: "Shirye-shiryen da jama’a suka gudanar, a Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma a Najaf, Karbala da hanyar tattakin Arba’in, sun gudana yadda ya kamata. Da daddare, jama’a suna taruwa da wuri a kan lokaci domin gudanar da aikinsu na kasancewa a fage cikin ƙwazo, suna ɗaga tutoci, suna rera taken nuna goyon baya, tare da gudanar da irin shirye-shiryen da ake yi a Jamhuriyar Musulunci ta Iran a can ma."

Wakilin Waliyyul Faƙih kan harkokin Hajji da Ziyara, yayin da yake ishara da halartar al’ummar Iraki a waɗannan shirye-shirye, ya ce: "Al’ummar Iraki, waɗanda suka nuna cikakken goyon bayansu a jana’izar, sun kuma taka muhimmiyar rawa a wannan gagarumin taro. A wasu daga cikin shirye-shiryen, ’yan’uwanmu ’yan Iraki sun kasance tare da masu ziyara ’yan Iran wajen ɗaga tutoci, sannan kuma suka halarci wannan shiri mai daraja da kulawa ta musamman."

Hujjatul Islam wal Muslimin Nawaab ya bayyana cewa Arba’in din bana yana da wasu kebantattun siffofi, inda ya ce: "Wannan shi ne karo na farko da aka gudanar da Arba’in ba tare da Shahidin Jagora a zahiri ba; duk da haka, ruhinsa mai girma, shawarwarinsa da jagorancin wannan ɗan shahidi sun kasance a cikin dukkan waɗannan shirye-shirye, yana nan yana lura da su. Al’ummar Jamhuriyar Musulunci ta Iran ma sun gudanar da ziyara a madadinsa, suna tunawa da shi da kuma tunawa da abubuwan da suka shafi rayuwarsa, tare da neman ɗaukar fansar jininsa. A cikin shirye-shirye daban-daban, a koyaushe ana magana game da kyawawan ɗabi’unsa, tafarkin rayuwarsa, shawarwarinsa da darussan da ya bayar, tare da bayyana muhimman bayanai ga jama’a."

Ya ci gaba da cewa: "Ɗaya daga cikin abubuwan da ya kamata a kula da su a bana fiye da shekarun baya shi ne cewa maƙiya ba sa son a riƙa ambaton sunan Shahidin Jagora, amma Allah yana kiyaye haskensa. A bana, sunansa, tuna shi da kalamansa sun yaɗu fiye da kowane lokaci, tare da taruwar jama’a fiye da kowane lokaci, kuma a faɗin ƙasa fiye da kowane lokaci a makwabciya kuma abokiyar Iran, wato Iraki. Jama’a suna ambatonsa cikin ƙauna da girmamawa."

Wakilin Waliyyul Faƙih kan harkokin Hajji da Ziyara ya ƙara da cewa: "Kamar yadda maƙiya suke son a sanya sunan gwamnatin Sahayoniya mai kisan yara ya zama sananne a duniya, amma al’ummomin duniya sun tattake tutar wannan gwamnatin mai kisan yara da kuma Amurka mai aikata laifuka, tare da ɗaga tutar Falasɗinu wadda suke son a manta da ita. Shekara bayan shekara, fagen kafirci yana ƙara fuskantar rashin nasara, yayin da fagen Musulunci da fagen gaskiya suke ci gaba da samun ci gaba, har zuwa lokacin da, da yardar Allah, sauran sassan duniya za su haskaka da hasken gaskiya, sannan a samar da duniya da babu zalunci da danniya ga dukkan bil’adama."

Yayin da yake magana kan wani ɓangare na shirye-shiryen Arba’in a ƙasar Iraki, ya ce: "Kamar yadda Jagoran Jamhuriyar Musulunci ya bayar da umarni, an gudanar da ziyara a madadin Shahidin Jagora. Baya ga ziyara a madadinsa, an kuma gudanar da ziyara domin tunawa da shahidai na yaƙe-yaƙen da aka tilasta wa Iran daga na farko zuwa na uku, da kuma waɗanda suka kasance a sahun gaba a fagen yaƙi da kuma tituna. Masu gabatar da jawabai ma sun jaddada wannan batu, yayin da jama’a cikin fahimta da basira suka mai da hankali kan wannan al’amari, suka gudanar da waɗannan shirye-shirye cikin ikhlasi."

A ƙarshe, Hujjatul Islam wal Muslimin Nawaab ya gode wa al’ummar Iraki, bisa jana’izar Shahidin Jagora mai cike da ɗaukaka, da kuma kyakkyawar hidimar da suka yi wa masu ziyarar Arba’in, inda ya ce: "Haƙiƙa, al’ummar Iraki sun yi iyakar abin da za su iya. Har ma an rawaito cewa wasu gwamnatocin wasu ƙasashe sun tambaye su dalilin da ya sa suka nuna irin wannan girmamawa da karramawa ga shugaban wata ƙasa daban. Sai suka amsa da cewa: “Shi (Shahidi Imam Khamenei) jagoran al’ummar Musulmi ne kuma ƙaunataccen mutum ne ga mutanen duniya masu ’yanci.”

Wannan magana tana nuna zurfin ƙauna da alaƙar da ke tsakanin al’ummomi Musulmi, da kuma babban matsayi na Wilaya da jagoranci a tsakanin al’ummar Musulmi da masu ’yanci na duniya.

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha